Bakonmu A Yau

Ibrahim Garba Wala kan tallafin man da Najeriya ta zuba na tiriliyan 7

Informações:

Sinopse

Gwamnatin Najeriya ta ce ta biya kusan naira tiriliyan 7 a matsayin tallafin man fetur a wani yunƙuri na ganin al'ummar ƙasar basu sayi man da tsada ba.  A cewar Gwamnatin namijin ƙoƙarin da ta yi wajen zuba wannan maƙuden kuɗaɗe su ne suka taimaka wajen hana hauhawar farashin man na fetur ta yadda har ta kai ana iya sayen man da sauƙi a yanzu.Sanarwar da gwamnatin Najeriyar ta fitar ta ce ta sanya wannan tallafi ne daga watan Agustan bara zuwa Disambar shekarar nan.Dangane da wannan Bashir Ibrahim Idris ya tattauna da Ibrahim Garba Wala ɗaya daga cikin masu fafutukar kare haƙƙin jama'a a ƙasar ga kuma yadda tattaunawarsu ta gudana.