Lafiya Jari Ce

Yadda cutar borin gishiri ke addabar mata masu juna biyu a Jamhuriyar Nijar

Informações:

Sinopse

A wannan makon shirin zai mayar da hankali kan cutar borin gishiri ko kuma kumburin da mata ke fama da ita yayin da suke da dauke da juna biyu, wacce kuma a lokuta da dama kan haddasa asarar rayuka. Wannan cuta a Jamhuriyar Nijar na daga cikin wacce ke ciwa hukumomi tuwo a kwarya ganin yadda mata sama da dari biyar da 30 cikin kowace mace dubu daya ne kamuwa da wannan cuta, kuma sama da 50 ke rasa ransu a sanadiyarta.  Ku latsa alamar sauti don sauraron cikakken shirin tare da Azima Bashir Aminu.....